DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta rage wutar lantarki da take sayarwa Jamhuriyar Nijar zuwa megawatts 46 daga megawatt 80

-

A wani rahoto da gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa ragin ya nuna an samu raguwar wutar lantarki da kashi 42 cikin dari ga kasar.

Ministan makamashi na Nijar, Haoua Amadou, ya ce matakin ya sa wutar lantarkin kasar ta ragu da kashi 30 zuwa 50 cikin 100, kuma ya tilasta wa kamfanin samar da wutar lantarki mallakar gwamnati Nigelec aiwatar da shirin rage wutar lantarki da ka iya daukar kwanaki da dama, musamman a birnin Yamai.

Nijeriya ta dakatar da fitar da wutar lantarkin da take fitarwa zuwa yankin yammacin Afirka a wani bangare na takunkumin da yankin ya kakaba wa gwamnatin mulkin soji da ta hambarar da shugaba Mohamed Bazoum a watan Yulin 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Mafi Shahara