Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya Bello Matawalle, ya yi watsi da ikirarin da masu sukar gwamnati ke yi cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba mai son ci gaban yankin Arewacin Nijeriya ne ba, yana mai cewa Shugaban kasar ya jajirce wajen magance dimbin kalubalen da yankin ke fuskanta.
A wata sanarwa da babban mataimakin ministan kan harkokin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fitar, Matawalle ya bayyana cewa dimokuradiyya ta samu gindin zama a Nijeriya karkashin Shugaba Tinubu fiye da kowane lokaci.
Ya ce masu yi masa kalaman na cewa Tinubu ba masoyin arewa ne ba, na amfani da farfaganda da karya ne don neman cimma muradunsu na siyasa.