Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Umar Iliya Damagum, ya yi watsi da ikirarin rikicin cikin gida a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa jam’iyyar PDP ta ci gaba da kasancewa a dunkule duk da rahotannin da kafafen yada labarai ke yaÉ—awa kan rikicin jam’iyyar.
Damagum ya bayyana cewa, jam’iyyar PDP a koda yaushe babbar jam’iyyar adawa ce, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ta san yadda za ta magance duk wata matsalarta ta cikin gida idan ta ta so.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da New Nigeria Peoples Party (NNPP) da suka koma PDP a kananan hukumomin Nguru da Bade a jihar Yobe.