DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wani rikicin da ya dabaibaye PDP, kan ‘ya’yanta hade yake – Damagum

-

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Umar Iliya Damagum, ya yi watsi da ikirarin rikicin cikin gida a cikin jam’iyyar, yana mai jaddada cewa jam’iyyar PDP ta ci gaba da kasancewa a dunkule duk da rahotannin da kafafen yada labarai ke yaÉ—awa kan rikicin jam’iyyar.

Damagum ya bayyana cewa, jam’iyyar PDP a koda yaushe babbar jam’iyyar adawa ce, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ta san yadda za ta magance duk wata matsalarta ta cikin gida idan ta ta so.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da New Nigeria Peoples Party (NNPP) da suka koma PDP a kananan hukumomin Nguru da Bade a jihar Yobe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara