DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

-

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a zaben 2027 mai zuwa.

Duk da cewa har yanzu Shugaba Tinubu bai kai rabin wa’adinsa na farko ba, kuma bai bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a hukumance ba, amma shugabannin jam’iyyar APC sun yi amfani da dandalin taron hadin kan babban birnin tarayya Abuja—wanda aka gudanar a filin wasa na Old Parade da ke Abuja, domin nuna goyon bayansu ga takararsa karo na biyu.

Google search engine

An shirya taron ne domin tarbar shugaban karamar hukumar Abuja Municipal Area Council (AMAC) Hon. Christopher Zakka Maikalagu, kansiloli, da dubban magoya bayansu sun shigo jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP.Da yake zantawa da manema labarai a wajen taron, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin maliya, ya bayyana kwarin gwiwar sake zaben Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara