Dakataccen Gwamnan jihar Rivers Siminalayi fubara ya yi kira ga mazauna jihar Rivers da su marawa shugaban kasa Bola Ahmad Tunubu baya musamman a shirinsa na “Renewed Hope Agenda”.H
akan na zuwa ne cikin sakonsa na bikin Ista, inda ya yi kira ga al’ummar jihar da su zauna lafiya domin Ista lokaci ne mai tsarki na sulhu da zaman lafiya.
Ya kuma jaddada sadaukarwarsa wajen gudanar da shugabanci na gari, yana mai tabbatarwa da ‘yan kasa cewa jihar za ta ci gaba da kawo sauyi a karkashin jagorancinsa.