DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar PDP a shirye take domin tunkarar zaben 2027 – Samuel Anyanwu

-

Sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Samuel Anyanwu, ya bayyana jin dadinsa da irin shirye-shiryen da jam’iyyar ke yi gabanin zabukan 2027 a jihar Imo da Nijeriya.

Anyanwu, ya bayyana hakan ne a karshen mako, lokacin da yake jawabi ga kwamitin zartarwar jam’iyyar PDP a jihar Imo, wanda ya hada da shugabanni da masu ruwa da tsaki a sakatariyar jam’iyyar a Owerri, jihar Imo.

Ya ce dole ne ‘ya’yan jam’iyyar su yi aiki kafada da kafada domin cimma burinsu na kwace mulki hannun APC, yana mai cewa zaben gwamna na da muhimmanci ga jam’iyyar domin karbar mulki a jihar Imo.

Anyanwu ya ce mutanen Imo sun gaji da yaudara da gwamnatin yanzu ke yi don haka akwai bukatar a tsaya kai da fata domin yin nasara a zabuka masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara