DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Filin jirgin saman Bola Tinubu dake Minna zai zama madadin filin jirgin saman Abuja duk lokacin da aka samu matsala – Gwamnatin Nijeriya

-

Gwamnatin tarayya ta ayyana filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu, dake Minna jihar Neja a matsayin madadin filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe na Abuja.

Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo ne ya bayyana haka a wajen ƙaddamar da tashi da saukar jiragen sama a filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu, inda jirgin sama na Overland Airways ya fara tashi.

Google search engine

Keyamo ya ce filin jirgin yana da tsari da yanayin da ya dace da kowane filin jirgin sama na kasa da kasa a fadin duniya, kuma za a rika amfani da shi a duk lokacin da aka samu cunkoson jirage ko wata matsala a filin jirgin sama na Abuja.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara