DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hisbah a Kano ta rushe wani wurin da ake yada jita-jitar an ga sahun Annabi

-

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta rushe wani wuri da ke a Dakata cikin kwaryar birnin, bayan bazuwar jita-jita cewa wurin na dauke da sawun kafa na fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.

Majiyar DCL Hausa ta jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa, wurin, da a kwana nan aka share domin gina layin dogo, ya ja hankalin dumbin mabiya addinin Musulunci bayan bayyanar wata alamar sawun kafa a cikin laka, tare da fitar ruwa daga wurin.

Google search engine

Jita-jitar da ta yadu cikin gaggawa cewa “Ruwan Albarka” na bubbuga a wurin kuma yana dauke da sawun Annabi, lamarin da ya sa mutane ke zuwa domin neman waraka da samun tubarraki.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Dr Mujahideen Aminudeen, ya gargadin jama’a da kada su yarda da irin wadannan labaran da ke jefa mutane a hanyar bata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara