DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hisbah a Kano ta rushe wani wurin da ake yada jita-jitar an ga sahun Annabi

-

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta rushe wani wuri da ke a Dakata cikin kwaryar birnin, bayan bazuwar jita-jita cewa wurin na dauke da sawun kafa na fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.

Majiyar DCL Hausa ta jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa, wurin, da a kwana nan aka share domin gina layin dogo, ya ja hankalin dumbin mabiya addinin Musulunci bayan bayyanar wata alamar sawun kafa a cikin laka, tare da fitar ruwa daga wurin.

Google search engine

Jita-jitar da ta yadu cikin gaggawa cewa “Ruwan Albarka” na bubbuga a wurin kuma yana dauke da sawun Annabi, lamarin da ya sa mutane ke zuwa domin neman waraka da samun tubarraki.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Dr Mujahideen Aminudeen, ya gargadin jama’a da kada su yarda da irin wadannan labaran da ke jefa mutane a hanyar bata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara