DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dakatattun ‘yan majalisar dokokin Zamfara sun ja daga tare da nada wani shugaban majalisa

-

‘Yan majalisar dokokin jihar Zamfara guda tara da aka dakatar, sun yi wani zaman majalisar dokoki tare da zabar sabon kakakin majalisa, lamarin da ke nuni da ruruwar wutar rikicin siyasar jihar.

‘Yan majalisar, wadanda aka dakatar a watan Fabrairun 2024 bisa zarginsu da rashin da’a, sun yi wani zama na farko a wani wuri da ba a bayyana ba a ranar Laraba, a cewar jaridar Dailytrust.

Google search engine

Yayin zaman sun zabi Hon. Bashir Aliyu Gummi a matsayin shugaba, haka kuma sun umurci Gwamna Dauda Lawal da ya sake gabatar da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 a gaban majalisar ta su.

Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Adamu Aliyu ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, inda ya jaddada bukatar daukar matakin ladabtarwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara