DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta ba da damar a kama tare da tsare wadanda suka tallata dandalin CBEX da ya wawure kudaden ‘yan Nijeriya

-

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta amince da bukatar Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati, ta kama tare da tsare wasu masu tallata shafin kudin Crypto na CBEX da ake zargin ya wawure kudaden da suka haura dala biliyan 1 na ‘yan Nijeriya.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya ba da umarnin ne, bayan ya saurari bayanai daga lauyar EFCC Fadila Yusuf.

Google search engine

Hukumar ta EFCC ta nemi izinin kotu domin ta kama wadanda ake zargin tallata wannan dandalin tare da tsare su, inda za ta ci gaba da bincike tare da shigar da kara.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Nijeriya ta zamo ta biyar a ƙasashen da suka fi ƙwarewa a harshen Turanci a nahiyar Afrika

A wani rahoto da EF SET na shekarar 2025 ta fitar kasar Afirka ta Kudu ce ta ke kan gaba a jerin ƙasashen Afirka wajen...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta ɗage komawar zaman majalisa zuwa 5 ga Maris

Majalisar Wakilan Nijeriya, ta ɗage komawar zaman majalisa daga Talata, 24 ga Fabrairu 2026, zuwa Alhamis, 5 ga Maris 2026. Sakataren Majalisar, Kamoru Ogunlana, ya bayyana...

Mafi Shahara