DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta ba da damar a kama tare da tsare wadanda suka tallata dandalin CBEX da ya wawure kudaden ‘yan Nijeriya

-

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta amince da bukatar Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati, ta kama tare da tsare wasu masu tallata shafin kudin Crypto na CBEX da ake zargin ya wawure kudaden da suka haura dala biliyan 1 na ‘yan Nijeriya.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya ba da umarnin ne, bayan ya saurari bayanai daga lauyar EFCC Fadila Yusuf.

Google search engine

Hukumar ta EFCC ta nemi izinin kotu domin ta kama wadanda ake zargin tallata wannan dandalin tare da tsare su, inda za ta ci gaba da bincike tare da shigar da kara.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mo Salah ya kafa tarihi a Firimiya inda ya zama dan wasa mafi ba da gudummuwar kwallaye a kulob daya

Dan wasan Liverpool, Mohamed Salah, ya karya tarihin mafi yawan gudummawar kwallaye (zura kwallo da bayarwa) da dan wasa ya taba yi wa kungiya daya...

Duk inda dan Nijeriya yake bai da wuyar ganewa saboda izza da kwarin guiwa a tafiyarsa da mu’amalarsa – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce ana iya gane dan Nijeriya a ko’ina cikin duniya, ciki har da London, saboda irin izza da kwarin...

Mafi Shahara