DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

-

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga cikin kasashen da Allah ya hore da albarkatun kasa.

Wannan na cikin rahoton Africa Pulse da aka fitar yayin taron asusun bada lamuni na duniya IMF da Bankin Duniya da ke gudana a birnin Washington D.C na Amurka.

Google search engine

Rahoton ya nuna cewa yankin Afrika ta Kudu da kasashen yankin Sahel (Sub-Saharan Africa) na da mafi yawan talakawa a duniya, inda kusan kaso 80 cikin 100 na talakawan duniya ke zaune a wannan yanki.

Najeriya na daga cikin kasashe hudu da ke dauke da rabin yawan talakawan da suka kai miliyan 560 a Afrika.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara