DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

-

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga cikin kasashen da Allah ya hore da albarkatun kasa.

Wannan na cikin rahoton Africa Pulse da aka fitar yayin taron asusun bada lamuni na duniya IMF da Bankin Duniya da ke gudana a birnin Washington D.C na Amurka.

Google search engine

Rahoton ya nuna cewa yankin Afrika ta Kudu da kasashen yankin Sahel (Sub-Saharan Africa) na da mafi yawan talakawa a duniya, inda kusan kaso 80 cikin 100 na talakawan duniya ke zaune a wannan yanki.

Najeriya na daga cikin kasashe hudu da ke dauke da rabin yawan talakawan da suka kai miliyan 560 a Afrika.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka biya kudin fansa, aka karbi kudin aka kuma ki sako mutanen a...

Dattawan al’ummar Gidan Waya da ke ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna sun bayyana cewa sun sayar da buhunan masara sama da 3,000 domin tara...

Sojoji sun amince an kitsa yunkurin juyin mulki kan Tinubu

Rundunar sojin Najeriya ta amince cewa wasu jami’anta sun kitsa yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne...

Mafi Shahara