DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

-

 

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, ko da ba tare da goyon bayan gwamnoni ba.

Google search engine

El-Rufai, wanda kwanan nan ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyar SDP, ya bayyana haka ne yayin wata hira da manema labarai a birnin Kano, inda ya ce dabarar da kawancen ke amfani da ita ita ce ta kai tsaye wajen tunkarar masu kada kuri’a, ba wai dogaro da masu rike da mukaman siyasa ba.

Wannan kalami na El-Rufai na zuwa ne a daidai lokacin da Kungiyar Gwamnonin PDP ta bayyana kin amincewa da kowacce irin hadaka ko kawance a kokarin yin maja da wasu jam’iyyun adawa ke yi kafin 2027.

Sai dai bayan taron da aka gudanar a Ibadan, karkashin jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Umar Damagum, da wasu gwamnoni, kungiyar ta nesanta kanta da wannan sabuwar tafiya, tana mai cewa jam’iyyar PDP za ta tsaya da kafafunta har zuwa 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara