An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya.
Ana dai sa ran fitar da wannan sakamako ne a ranar Juma’a mai zuwa 2 ga watan Mayun, 2025 kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.
Bangarorin da suka yi binciken da suka haÉ—a da FBI, IRS, DEA da CIA za su fitar da sakamakon binciken ne kamar yadda kotu ta umurta.
Ana dai zargin cewa binciken na da nasaba da miyagun kwayoyi wanda ya shafi Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya tun a cikin shekarun 1990.