Tsohon mai ba shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da shugaban kasa mai ci, Bola Tinubu, da su janye daga aniyarsu ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027, tare da ba matasa masu kwarewa damar jagorantar kasa.
A wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels Television, Baba-Ahmed ya bayyana cewa Atiku ya tsaya takarar shugaban kasa har sau shida ba tare da nasara ba, don haka ya kamata ya janye ya kuma tallafa wa matasa masu tasowa.
Haka kuma, Baba-Ahmed ya shawarci Tinubu da kada ya nemi wa’adi na biyu a 2027, yana mai cewa ya kamata ya Yi amfani da sauran lokacin mulkinsa wajen gyara kasa da kuma horar da matasa da za su gaje shi.