DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kada ka sake tsayawa takarar shugabancin Nijeriya – Shawarar Hakeem Baba Ahmed ga Atiku Abubakar

-

Tsohon mai ba shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da shugaban kasa mai ci, Bola Tinubu, da su janye daga aniyarsu ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027, tare da ba matasa masu kwarewa damar jagorantar kasa.

A wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels Television, Baba-Ahmed ya bayyana cewa Atiku ya tsaya takarar shugaban kasa har sau shida ba tare da nasara ba, don haka ya kamata ya janye ya kuma tallafa wa matasa masu tasowa.

Haka kuma, Baba-Ahmed ya shawarci Tinubu da kada ya nemi wa’adi na biyu a 2027, yana mai cewa ya kamata ya Yi amfani da sauran lokacin mulkinsa wajen gyara kasa da kuma horar da matasa da za su gaje shi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara