DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NELFund sun musanta karkatar da kudaden bashin karatun dalibai 

-

Shirin ba da bashin karatu na Najeriya NELFund ya musanta zargin karkatar da kudaden da aka bai wa dalibai.

Wannan dai na zuwa ne bayan da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta ce tana gudanar da bincike kan zargin almundahana a yayin raba kudaden.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na asusun, Oseyemi Oluwatuyi, NELFund ya fitar, ya ce an yi wa kalaman ICPC gurguwar fahimta ne.

A gefe guda hukumar ta ICPC ta yi karin haske kan bayanin da ta yi a baya game da bashin karatun daliban.

Mai magana da yawun hukumar, Demola Bakare, ya ce hukumar za ta yi bincike kan yadda aka kashe kudade ne da suka kai biliyan 100 saboda bayanan da ta samu cewa makarantu 51 sun karkatar da kudaden ba bisa ka’ida ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara