DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NELFund sun musanta karkatar da kudaden bashin karatun dalibai 

-

Shirin ba da bashin karatu na Najeriya NELFund ya musanta zargin karkatar da kudaden da aka bai wa dalibai.

Wannan dai na zuwa ne bayan da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta ce tana gudanar da bincike kan zargin almundahana a yayin raba kudaden.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na asusun, Oseyemi Oluwatuyi, NELFund ya fitar, ya ce an yi wa kalaman ICPC gurguwar fahimta ne.

A gefe guda hukumar ta ICPC ta yi karin haske kan bayanin da ta yi a baya game da bashin karatun daliban.

Mai magana da yawun hukumar, Demola Bakare, ya ce hukumar za ta yi bincike kan yadda aka kashe kudade ne da suka kai biliyan 100 saboda bayanan da ta samu cewa makarantu 51 sun karkatar da kudaden ba bisa ka’ida ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin dakatar da babban taronta a Ibadan

Jam’iyyar PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin kotun tarayya da ta dakatar da gudanar da babban taronta da aka shirya yi a...

Matatar man Dangote ta yi alkawarin samar da wadataccen man fetur a lokacin bukukuwan karshen shekara

Matatar man Dangote ta tabbatar da cewa za ta samar da isasshen man fetur da dizal a fadin Nijeriya a lokacin bukukuwan karshen shekara domin...

Mafi Shahara