DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An fadi dalilin da ya sa dan sandan da ke yi wa Ganduje dogari ya sunkuya ya daura masa takalma a kafa

-

Mataimaki na Musamman ga shugaban jam’iyyar APC na kasa, kan harkokin sadarwa Aminu Dahiru Ahmad, ya kare dan sanda da aka gani yana daura wa shugaban jam’iyya takalmi.

Bidiyon da ya nuna dan sandan a duke gaban Ganduje yana daura masa takalmi ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Google search engine

Aminu Dahiru Ahmad ya ce shaidun gani da ido sun tabbatar cewa dan sandan ya kai dauki ga takalman Ganduje ne domin tabbatar da tsaron lafiyarsa.

Ya ce sabanin abin da wasu ke yayatawa, Ganduje yana girmama masu taimaka masa da ma’aikatan gidansa matuka.

Aminu Dahiru ya ce, wannan gajeren bidiyo dai shaida ce da ke nuna yadda kyakkyawar alaka take tsakanin Dr Abdullahi Umar Ganduje da masu taimaka masa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara