DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An fadi dalilin da ya sa dan sandan da ke yi wa Ganduje dogari ya sunkuya ya daura masa takalma a kafa

-

Mataimaki na Musamman ga shugaban jam’iyyar APC na kasa, kan harkokin sadarwa Aminu Dahiru Ahmad, ya kare dan sanda da aka gani yana daura wa shugaban jam’iyya takalmi.

Bidiyon da ya nuna dan sandan a duke gaban Ganduje yana daura masa takalmi ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Aminu Dahiru Ahmad ya ce shaidun gani da ido sun tabbatar cewa dan sandan ya kai dauki ga takalman Ganduje ne domin tabbatar da tsaron lafiyarsa.

Ya ce sabanin abin da wasu ke yayatawa, Ganduje yana girmama masu taimaka masa da ma’aikatan gidansa matuka.

Aminu Dahiru ya ce, wannan gajeren bidiyo dai shaida ce da ke nuna yadda kyakkyawar alaka take tsakanin Dr Abdullahi Umar Ganduje da masu taimaka masa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara