DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata mata ta gurfana gaban kotu a Kano bayan da aka zarge ta da auren maza biyu lokaci daya

-

An gurfanar da wata mata a gaban Kotun shari’ar musulunci da ke Post Office a cikin birnin Kano bisa zargin auren maza biyu a lokaci guda.

Harira Muhammad Tudun Murtala da mijinta na farko, Sagiru Shuaibu Tudun Murtala, sun yi aure na tsawon watanni shida suna kuma zaune kowa da gidansa kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Lokacin da mijin nata na farko ya ziyarce ta ne ya tarar da wani namiji a dakin matarsa, inda ya sanar da makwabta abin da ke faruwa.

Lokacin da ta bayyana a gaban kotu, matar da farko ta musanta cewa tana aure da mijinta na farko, amma da alkalin kotun ya umurci ta rantse da Alkur’ani, sai ta daina jan maganar.

Mijin na biyu, Bello Abdullahi Yankaba, ya shaida wa kotu cewa kawunta, wani Abdullahi Umar, ne ya daura aure tsakaninsu bayan ya biya sadaki na Naira dubu dari.

Alkalin kotun, Khadi Munzali Tanko Soron Dinki, ya bayar da umurnin ci gaba da bincike daga ‘yan sanda tare da ba da umurni a ci gaba da tsare matar da mijinta na biyu har zuwa ranar 16 ga Mayu a gidan gyaran hali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar wakilai 8 na LP da PDP sun sauya sheka a jihohin Delta da Enugu

A ranar Talata ‘yan majalisar wakilai takwas suka bayyana ficewa daga jam’iyyunsu zuwa wasu jam'iyyu daban-daban. ‘Yan majalisar wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga...

Gwamnatin tarayya ta fito da tsarin da zai kawo karshen wahalar da ake sha wajen tantance lambar NIN 

Gwamnatin tarayya ta amince da wani sabon tsari da hukumar dake bayar da katin dan kasa za ta rika amfani da shi don saukaka tantance...

Mafi Shahara