DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bello Turji na cikin matsin lamba daga sojojin Nijeriya – Minista Badaru

-

Ministan Tsaro na Najeriya, Muhammad Badaru, ya bayyana cewa shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji yana gudun hijira sakamakon hare-haren da sojojin Najeriya ke kai wa a ‘yan kwanakin nan.

A cewarsa, rundunar soji ta samu nasarar kashe wasu daga cikin manyan shugabannin ‘yan ta’adda da suka hada da:

Google search engine

Maza Barume Madaro da Kachalla Alhaji Dati da Bani Wala Burki da Kachalla Dogo Kwaden da Chairman Hanazuma sai kuma Kachalla Bandiyo da Maiyara Madaci da sauransu.

Minista Badaru ya ce dakarun soji na ci gaba da murkushe ‘yan ta’adda, kuma yawancin shugabanninsu suna cikin firgici da gudu.

Ya kara da cewa sojoji na kara kaimi wajen tattara bayanan sirri domin hana hare-haren ta’addanci kafin su faru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara