DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar SON ta kama tayoyi da wayoyin lantarki na jabu a Nijeriya

-

Hukumar SON mai kula da ingancin kaya a Nijeriya ta ja hankalin cewa akwai tayoyi da wayoyin lantarki marasa inganci da ke yawo cikin kasar.

Babban daraktan hukumar Dr Ifeanyi Chukwunonso Okeke ne ya bayyana damuwarsa da wannan lamari a lokacin da ya jagoranci lalata wasu tayoyi da wayoyin lantarki da wasu kayayyaki marasa inganci da kimarsu ta kai ta bilyoyin Naira a jihar Legas, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Ya koka kan yadda ake samun karuwar kaya marasa inganci da kuma na jabu a manyan kasuwannin da ke fadin kasar, tare da zargin wasu da ya kira masu zagon kasa ga tattalin arzikin kasa da daukar alhakin shigo da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara