DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa uku daga jihar Katsina sun bar PDP sun koma APC

-

‘Yan majalisar wakila uku daga jihar Katsina sun bar jam’iyyarsu ta PDP sun koma APC.

‘Yan majalisar su ne Ali Iliyasu na Safana/Batsari/Danmusa, Salisu Yusuf Majigiri na Mashi/Dutsi da Abdullahi Balarabe na Bakori/Danja.

Kakakin majalisar wakilan Tajuddeen Abbas ne ya karanta sanarwar ficewar ta su.

‘Yan majalisar dai sun bayyana rikicin da ya addabi jam’iyyar PDP ne ya sa suka bar ta. Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya ziyarci majalisar don gane wa idonsa yadda ‘yan majalisar suka sauya sheka suka koma jam’iyya mai mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara