Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMajalisar sarakunan Idoma ta soke sarautar da aka bai wa Shugaba Tinubu

Majalisar sarakunan Idoma ta soke sarautar da aka bai wa Shugaba Tinubu

Majalisar gargajiya ta Idoma ta soke sarautar gargajiya da aka bai wa Shugaba Bola Tinubu da wasu mutane hudu a lokacin bikin Igede Agba na Oju, Jihar Benue.

A cewar sanarwar da sakataren majalisar, Mista Adegbe Uloko, ya fitar ranar Litinin, an ce karramawar da aka yi wa Tinubu da sauran manyan baki ya saba da umarnin da majalisar ta fitar tun ranar 2 ga Satumba, 2025, na dakatar da bayar da sarautun gargajiya a kasar Idoma.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, ne ya karɓi sarautar a madadin Shugaba Tinubu daga hannun Adiharu na Igede, Mai Martaba CP Oga Ero (mai ritaya), a yayin bikin ranar Asabar.

Sai dai, majalisar ta bayyana cewa wannan karramawar ta sabawa tsarin da aka shimfiɗa, kuma ta ce sarautun da aka bai wa Tinubu da sauran manyan baki sun tashi aiki.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata