Majalisar gargajiya ta Idoma ta soke sarautar gargajiya da aka bai wa Shugaba Bola Tinubu da wasu mutane hudu a lokacin bikin Igede Agba na Oju, Jihar Benue.
A cewar sanarwar da sakataren majalisar, Mista Adegbe Uloko, ya fitar ranar Litinin, an ce karramawar da aka yi wa Tinubu da sauran manyan baki ya saba da umarnin da majalisar ta fitar tun ranar 2 ga Satumba, 2025, na dakatar da bayar da sarautun gargajiya a kasar Idoma.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume, ne ya karɓi sarautar a madadin Shugaba Tinubu daga hannun Adiharu na Igede, Mai Martaba CP Oga Ero (mai ritaya), a yayin bikin ranar Asabar.
Sai dai, majalisar ta bayyana cewa wannan karramawar ta sabawa tsarin da aka shimfiɗa, kuma ta ce sarautun da aka bai wa Tinubu da sauran manyan baki sun tashi aiki.
Majalisar sarakunan Idoma ta soke sarautar da aka bai wa Shugaba Tinubu
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
