Gwamnonin jihohi 19 na Arewa na taro a Kaduna domin tattaunawa kan matsalolin tsaro da suka kunshi sace-sace, kai hare-haren ’yan bindiga da kuma karuwar tashe-tashen hankula a yankin.
Jaridar Punch ta rawaito cewa taron ya mayar da hankali wajen gano sababbin dabaru da matakan gaggawa da za su rage yawaitar hare-haren, tare da kawo karshen ta’addanci da ke addabar al’ummar yankin Arewa.
Masu shirya taron sun bayyana cewa tattaunawar ta haɗa da sabunta dabarun hadin gwiwa tsakanin jihohi, da kuma bullo da ingantattun hanyoyin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
