Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun saki matashi da mata da suka sace a Abuja

‘Yan bindiga sun saki matashi da mata da suka sace a Abuja

‘Yan bindiga sun saki wani yaro mai shekaru 15 da kuma ’yan mata shida da suka yi garkuwa da su a kauyen Gidan Bijimi da ke Kawu, a karamar hukumar Bwari ta Abuja, bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan biyu daga iyalansu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar, dauke da makamai, sun kai farmaki kauyen ne a daren Laraba da misalin ƙarfe 9:30 na dare, inda suka yi awon gaba da mutanen yayin da suka kasa kama wanda suke nema Thomas Waha Sarki.

Wadanda aka sako sun haɗa da Blessing Awu, Abigail Kasabare, Asabe Joshua, Kankani Joshua, Talatu Jaba, Agnes Kasabare da David Awu.

An sako su ne a daren Asabar a dajin Kuyeri da ke cikin ƙaramar hukumar Kagarko a jihar Kaduna, inda aka kai kuɗin fansar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata