DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Arewa za su tara Naira biliyan 228 don yakar matsalar tsaro

-

Gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya sun bukaci a dakatar da hakar ma’adanai a yankin na tsawon watanni shida, suna bayyana shi a matsayin babban dalilin ta’azzarar matsalolin tsaro a yankin.

 

Google search engine

Wannan ya biyo bayan wani taro da suka gudanar a ranar Litinin, domin tattaunawa kan yadda za a shawo kan matsalar.

 

Kazalika sun bayyana shirin bude asusu wanda za su tara Naira biliyan 228 don inganta yakinsu da matsalar.

 

Karkashin shirin dai, kowace jiha da kananan hukumominta za su rika bayar da Naira biliyan 1 a kowane wata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara