Rundunar ta ce hakan ya fito ne sakamakon taɓarɓarewar tsaro da har ta kai ga Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a ƙasar.
An bayyana cewa fiye da mutane 600 aka yi garkuwa da su a watan Nuwamba kaɗai, ciki har da ɗalibai sama da 300 a Jihar Neja, masu ibada 38 a Kwara, da ɗalibai 25 a Kebbi.
Bayan haka ne Shugaba Tinubu ya umarci ƙara yawan jami’an tsaro da kuma tura karin ma’aikata zuwa jihohi.
A cikin wata takarda ta ciki, mai ɗauke da sa hannun Manjo Janar E. I. Okoro a ranar 3 ga Disamba, rundunar ta ce dakatar da ritaya na nufin karfafa aiki yayin da ake faɗaɗa yawan sojoji domin tunkarar matsalar tsaro.
