Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaZa'a sanya cibiyoyin lafiya a aikin titin Lagos–Calabar - Minista Dave Umahi

Za’a sanya cibiyoyin lafiya a aikin titin Lagos–Calabar – Minista Dave Umahi

Ministan Ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa sabon titin Lagos–Calabar zai kasance da wuraren hutu, hasken fitilu masu aiki da hasken rana, da kuma CCTV domin kara tsaro da kuma bada agajin gaggawa cikin mintuna goma kacal.

Umahi ya yi wannan bayani ne yayin duba aikin Calabar–Itu da sassan 3A da 3B na cikin kilomita 71.4 da ake ci gaba da ginawa a Cross River.

Aikin yana gudana ne ta karkashin kamfanin HITECH Africa, wanda ke amfani da fasahar reinforced concrete pavement (wato kankare).

Jaridar Punch ta ruwaito shi ya kara jinjinawa Shugaban Kasa Bola Tinubu, wanda ya farfado da aiki da ya tsaya tun shekaru fiye da 27 da suka wuce.

Shugaban HITECH, Dany Aboud, ya tabbatar da cewa za su kara ma’aikata da kayan aiki domin kammala aikin cikin watanni 36.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata