Tuesday, April 7, 2026
HomeSiyasaDa alamu matsalar tsaro ta fi karfin gwamnatin Nijeriya - Kwankwaso

Da alamu matsalar tsaro ta fi karfin gwamnatin Nijeriya – Kwankwaso

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce halin da ake ciki ya nuna Gwamnatin Nijeriya ta gaza a kokarinta na magance matsalolin tsaro a ƙasar.

Kwankwaso ya fadi hakan ne cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce dakile rashin tsaro babban nauyin gwamnati ne tare da jihohi da ƙananan hukumomi, amma yadda ake tafiyar da al’amura ya nuna gwamnati na samun tangarɗa.

Ya yi suka kan yadda jihohi ke kafa kungiyoyin sa-kai masu ƙarancin horo, yana cewa hakan na kawo yawaitar makamai a hannun jama’a.

Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan karuwar tsangwama da nuna bambanci na kabilanci, inda ya ce ana kama mutane ba bisa ka’ida ba a wasu yankuna, abun da ke rura ƙiyayya a kafafen sada zumunta.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata