Tsohon Ministan Shari’a na Nijeriya, Abubakar Malami, na tsare a hannun EFCC bayan an gayyace shi makon jiya kan wasu mu’amaloli da suka shafi dawo da wani ɓangare na kudin Abacha.
Rahoton jaridar Daily Trust ya gano cewa Malami ya musanta duk wani hannu a cikin lamarin, yana mai cewa bai san kome ba kuma bai aikata laifi ba.
A cikin wata sanarwa, ya ce shekaru da ya shafe a matsayin Babban Lauyan gwamnatin tarayya kuma Ministan Shari’a ya yi aikinsa ne wajen ƙarfafa yaki da harkokin ta’addanci da daukar nauyin ta’adda a kasar.
Malami ya bayyana cewa labarin kage ne kuma an yi amfani da shi wajen siyasa da nufin bata masa suna.
