Tuesday, April 7, 2026
HomeKetareAmurka damu matuka da hallin da ‘yan gudun hijira ke ciki a...

Amurka damu matuka da hallin da ‘yan gudun hijira ke ciki a Najeriya

Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilan Amurka ya sake jaddada ƙudirin Amurka na yaƙi da cin zarafin addini a duniya, musamman a Najeriya.

Jaridar Punch ta Ambato wata sanarwa da suka wallafa a shafinsu na X a ranar Laraba, sun ce Amurka ba za ta yi shiru ba yayin da ake kashe rayuka ba gaira ba dalili.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar da tawagar ‘yan majalisar Amurka ƙarƙashin jagorancin Riley Moore suka kai Najeriya bisa umarnin Shugaba Donald Trump.

Mai ba shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya tabbatar da cewa ziyarar ta mayar da hankali kan ƙarfafa haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, inganta tsaro a yankin, da kuma karfafa dangantakar tsaro tsakanin Najeriya da Amurka.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata