Tuesday, April 7, 2026
HomeKetareNijeriya ce a gaba cikin kasashen da ke karan tsaye ga hukuncin kotun ECOWAS

Nijeriya ce a gaba cikin kasashen da ke karan tsaye ga hukuncin kotun ECOWAS

Najeriya ce a sahun gaba na mafi yawan hukuncin Kotun ECOWAS da ba a aiwatar ba, a cewar alkaluman da Mataimakin Babban Rijistaran Kotun, Gaye Sowe, ya gabatar yayin bikin Ranar Kare Hakkokin Dan Adam ta Duniya a ranar Laraba.

Sowe ya bayyana cewa Najeriya na da hukunci 50 da har yanzu ba a aiwatar da su ba, cikin jimillar 125 na shari’u da kotun ta yanke kan ƙasar.

Inda ya ce wannan na nuna matsalar rashin bin hukunci a ƙasashe da dama na yankin.

Jaridar Punch ta Ambato shi na bayyana cewa tun kafuwar Kotun ECOWAS, ta yanke hukunci 492 kan ƙasashe mambobi 12, inda 192 daga ciki suka kasance masu bukatar aiwatarwa kai tsaye. A halin yanzu akwai shari’u 136 da ke jiran hukunci.

A bayanin rabon ƙasashe, Sowe ya ce kasashen Benin, Cape Verde, Côte d’Ivoire, Ghana, Guinea, Senegal, Sierra Leone da Togo suma na da tarin hukuncin da ba su aiwatar ba. Amma Najeriya ce ta fi yawan adadin.

Shugaban Kotun ta ECOWAS, Ricardo Gonçalves, ya ce duk da yanke muhimmam hukunci kan ’yancin rayuwa, ’yancin bayyana ra’ayi, taro, ilimi da sauran su, ƙasashe da dama sun kasa aiwatar da su, lamarin da ke tauye ingancin kare hakkin dan adam a yankin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata