Tuesday, April 7, 2026
HomeKetareNijeriya ta fara sulhu da Burkina Faso kan batun sojojinta

Nijeriya ta fara sulhu da Burkina Faso kan batun sojojinta

Gwamnatin Nijeriya ta fara tattaunawar diflomasiyya domin kubutar da sojojin Najeriya da jirgin saman yaƙin kasar C-130 da gwamnatin sojin Burkina Faso ta tsare saboda zargin karya dokar shiga sararin samaniyarta.

Sojojin da jirgin, waɗanda ake tsare da su tsawon kwanaki uku, sun ci gaba da kasancewa a hannun hukumomin Burkina Faso, inda majiyoyin soji suka tabbatar cewa Ma’aikatar Harkokin Waje ce yanzu ke jagorantar lamarin.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Kakakin ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa, ne ya tabbatar da yadda ofishin jakadancin Najeriya a Ouagadougou ya fara tattaunawa da hukumomin ƙasar domin ganin an saki dakarun da jirgin.

A bangaren Burkina Faso, hukumar labarai ta ƙasa ta sanar cewa an tilasta jirgin na NAF dauke da sojoji 11 yin saukar gaggawa bayan zargin karya dokar shiga sararin samaniya, lamarin da ƙungiyar AES ta kira take hakkinsu na ikon ƙasa.

Rundunar Sojin Saman Najeriya ta ce sojojin da ke cikin jirgin suna cikin koshin lafiya, tana mai bayyana cewa jirgin ya sauka ne a Bobo-Dioulasso bayan gano matsalar na’ura jim kadan bayan tashi daga Legas.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata