Gwamnatin jihar Katsina ta ce ta haramta yawan rufe lambar mota ba bisa ka’ida ba, lamarin da ta ce barazana ce ga tsaron jihar. Gwamnatin ta ce ana kara yawaita rufe lambar a kan motocin manyan jami’a da wasu mutane, abin da ka iya bai wa miyagu damar aikata laifi cikin sauƙi.
A kan haka ne Gwamna Dikko Umaru Radda ya umurci Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Katsina tare da sauran hukumomin kula da zirga-zirga su ɗauki mataki domin magance lamarin da kuma tabbatar da tsaron al’umma.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnati na Jiha, Abdullahi Garba Faskari, ya sanya wa hannu, gwamnatin ta shawarci jama’a su daina wannan dabi’a domin kauce wa kamawa da gurfanar da su gaban kotu.
