A wata wasika da shugaban Nijeriyar ya aike wa Majalisar Dattawa a cikin makon nan, Tinubu ya bukaci sanatoci su amince masa ya nada Aisha Mahmoud Kanti-Bello da Fouad Animashaun a matsayin kwamishinonin hukumar ta NERC mai kula da harkokin lantarki, amma ba a ga sunan Abdullahi Ramat a cikin wasikar ba.
Jaridar Daily Trust ta ce Tinubu ya shaida wa yan majalisar cewa sabuwar wasikar da ya turo musu ta shafe tsohuwar wasikar da ya tura musu a watan Agusta wadda ke dauke da sunan dan siyasar na jihar Kano.
