Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaTinubu ya fasa bai wa Abdullahi Ramat mukamin shugabancin hukumar NERC?

Tinubu ya fasa bai wa Abdullahi Ramat mukamin shugabancin hukumar NERC?

A wata wasika da shugaban Nijeriyar ya aike wa Majalisar Dattawa a cikin makon nan, Tinubu ya bukaci sanatoci su amince masa ya nada Aisha Mahmoud Kanti-Bello da Fouad Animashaun a matsayin kwamishinonin hukumar ta NERC mai kula da harkokin lantarki, amma ba a ga sunan Abdullahi Ramat a cikin wasikar ba.
Jaridar Daily Trust ta ce Tinubu ya shaida wa yan majalisar cewa sabuwar wasikar da ya turo musu ta shafe tsohuwar wasikar da ya tura musu a watan Agusta wadda ke dauke da sunan dan siyasar na jihar Kano.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata