Monday, April 6, 2026
HomeKetareAmurka ta gama hada rahoton binciken zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

Amurka ta gama hada rahoton binciken zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

Tawagar majalisar dokokin Amurka karkashin Riley Moore ta kammala bincike a Nijeriya kan zargin kisan Kiristoci, musamman a Benue, kuma za ta gabatar wa Shugaba Donald Trump da cikakken rahoto kafin ƙarshen Disambar nan.

Tawagar ta gana da ’yan gudun hijira, shugabannin Kiristoci, sarakunan gargajiya da manyan jami’an gwamnati, inda Moore ya ce sun ji labarai masu tayar da hankali game da hare-haren da ake zargin Fulani da masu tsattsauran ra’ayin addini suka yi.

Sai dai jaridar Daily Trust ta ambato yadda gwamnatin Nijeriya ta ce rikicin ba na addini ba ne, batu ne da ya fi karkata ga sauyin yanayi da kabila.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata