Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKo da za a ba ni Dala biliyan 1 ba zai ja...

Ko da za a ba ni Dala biliyan 1 ba zai ja ra’ayina shiga siyasa ba – Limamin wani coci a Nijeriya

Babban limamin Cocin Living Faith Church Worldwide (Winners Chapel), Bishop David Oyedepo, ya ce ba zai shiga siyasa ba ko da an ba shi dala biliyan ɗaya, yana mai jaddada cewa siyasa ba ta cikin kiran da Allah ya yi masa.

Oyedepo ya faɗi hakan ne a yayin taron Shiloh 2025 a Canaanland, Ota, Jihar Ogun, inda ya shawarci mambobin cocin su maida hankali kan kiran da Allah ya ba su.

A cewarsa, a shekarar 2015 na gargadi coci cewa wahala na tafe kuma wahalar ta zo.

Oyedepo ya ce Shiloh 2025, wanda ya fara ranar 9 ga Disamba kuma zai ƙare 14 ga watan, na nufin ƙarfafa bangaskiya da shirya mabiya don tasiri mai kyau ga al’umma.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata