Sunday, April 5, 2026
HomeKetareHukumomin Bénin na zargin Togo da ba wa jagoran juyin mulkin da...

Hukumomin Bénin na zargin Togo da ba wa jagoran juyin mulkin da bai yi nasara ba mafaka

Kwanaki shida bayan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a kasar Bénin, rahotanni sun nuna har yanzu ba a san inda laftanal kanal Pascal Tigri madugun juyin mulkin yake ba

Sai dai a wani rahoto da jaridar Jeune Afrique ta wallafa ta ce akwai yiwuwar cewa laftanal kanal Pascal Tigri yana kasar Togo, zargin da hukumomin Togo ba su karyata ko tabbatar da shi ba.

Dama dangantakar da ke tsakanin kasashen tana tangarda sakamakon wadansu matsaloli da suka wakana a tsakaninsu da suka hada da na bambancin ra’ayi akan kungiyar AES wacce kasar Togo ke nuna tana tare da ita har ma ta yi ikirarin yiwuwar shiga cikin ta yayin da kuma Bénin ke nuna adawa da kungiyar har ta kasance a sahu na gaba-gaba a kan matakin ECOWAS na kai wa Nijar hari a lokacin da sojoji suka yi wa Bazoum juyin mulki

Kazalika, wani dan majalisar dokokin kasar Bénin ya bayyana cewa a 2021, an masa tayin biliyoyin kudade na CFA daga kasar Togo dan ya bada hadin kai wajen tsara juyin mulki a Bénin

A yanzu haka kuma, ko baya ga Pascal Tigri da ake zargin yana samun mafaka a Togo, da dama daga cikin masu adawa da gwamnatin Bénin da ‘yan fafutukar masu sukar gwamnatin Talon na samun mafaka a Togon

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata