Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMinistocin kasashen ECOWAS sun yi bitar barazanar tsaro da inganta tattalin arziki...

Ministocin kasashen ECOWAS sun yi bitar barazanar tsaro da inganta tattalin arziki a taron kungiyar

Taron Ministocin ECOWAS karo na 95 ya kammala a Abuja bayan kwanaki na tattaunawa kan matsalolin tsaro, siyasa da tattalin arziki a yankin Yammacin Afirka.

A taron da aka gudanar daga 10 zuwa 12 ga watan Disamba, ministocin sun tattauna barazanar ta’addanci a yankin Sahel, yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba, laifuffukan ƙetare ƙasashe, matsalar tsaron teku a Tekun Guinea, da kuma juyin mulkin da ba bisa tsarin dimokuraɗiyya ba.

Da yake jawabin rufe taron, Ministan Harkokin Wajen Saliyo, Timothy Kabba, ya ce ECOWAS ta jaddada cewa dimokuraɗiyya, bin doka da oda, da tsarin mulki na gaskiya ba za su zama abin sulhu ba, yana mai cewa haɗin kai ne makamin yankin wajen shawo kan kalubalen da ke gabansa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata