DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu dauke da cutar HIV miliyan 1.6 ne daga cikin mutum miliyan 2 ne ke karbar magani a Nijeriya

-

Shugaban hukumar da ke yaki da cuta mai karya garkuwa jiki a Nijeriya Dr Temitope Ilori, ta ce akalla mutum miliyan 1.6 ne daga cikin mutane miliyan biyu dake fama da cuta mai karya garkuwar jiki ta HIV, ke karbar magani a Nijeriya.
Dr Temitope Ilori, ta ce wannan cutar ta fi kama wadanda ke tsakanin shekaru 15 zuwa 65, kuma karfin yaduwarta a kasar yana kashi 1.4
Ta bayyana hakan ne a wurin wani taro da aka shirya gabanin bukin ranar yaki da cutar AIDS da ya gudana a Abuja.
An ware ranar 1 ga watan Disamban kowace shekara ne domin wayar da kan al’ummar duniya akan irin hadarin wannan cutar tare da karfafawa wadanda ke rayuwa da wannan cutar mai karya garkuwar jiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara