Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamitin ba da shawara kan harkokin addini, tare da haɗin gwiwar kwamitin duban wata suka fitar a ranar Asabar, 20 ga Disamba, 2025.
Sanarwar ta bayyana cewa ba a samu rahoton ganin jinjirin watan Rajab ba daga ko ina a fadin Nijeriya a daren Asabar wanda ya yi daidai da 29 ga watan Jumada Sani, don haka watan ya cika kwana 30.
Sakamakon haka, Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya amince da rahoton tare da ayyana Litinin a matsayin 1 ga watan Rajab.
