Wednesday, April 8, 2026
HomeLabarai'Yan sanda sun kama wata mata a ake zargi da garkuwa da...

‘Yan sanda sun kama wata mata a ake zargi da garkuwa da kanta

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta cafke wata matar aure mai shekaru 26 tare da wani mutum mai shekaru 30, bisa zargin yin garkuwa da kanta da neman kudin fansa miliyan 2.5 daga hannun mijinta.

Mai magana da yawun rundunar DSP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke mutanen a wata sanarwa da ta fitar a Legas, inda ta ce rundunar ta samu kiran gaggawa a 24 ga watan Nuwamba daga wajen mijin matar, inda ya ce an sace matarsa.

Ta ce an sanar da ‘yansanda cewa masu garkuwar sun fara neman kudin fansa Naira miliyan 10, daga bisani suka rage zuwa Naira miliyan 3, kuma bayan biyan Naira miliyan 2.5, ba a saki matar ba, lamarin da ya sa rundunar ta tura jami’anta don bincike,inda a nan ne suka gano abinda ake zargi a kanta.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata