Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMajalisar Dattawan Nijeriya ta fara muhawara kan kasafin kudin 2026 na Nairan...

Majalisar Dattawan Nijeriya ta fara muhawara kan kasafin kudin 2026 na Nairan tiriliyan 58

Majalisar Dattawan Nijeriya ta fara muhawara kan kasafin kuɗin shekarar 2026, inda shugaban masu rinjaye, Sanata Opeyemi Bamidele daga Ekiti Ta Tsakiya, ya jagoranci tattaunawar kan kudirin da ke neman amincewa da kashe kuɗin har tiriliyan ₦58.47 a shekarar 2026.

Sanata Bamidele ya bayyana hakan ne a zaman majalisar ranar Talata, yana mai cewa kudirin shi ne zai ba da damar aiwatar da kasafin kuɗin 2026 da Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa Majalisar Ƙasa baki ɗaya a ranar 19 ga Disamba, 2025, wanda a dalilin haka aka ɗauka cewa ya riga ya tsallake karatu na farko.

A cewarsa, dokar kasafin kuɗin tana da matuƙar muhimmanci wajen tafiyar da mulki da kula da tattalin arziki, domin tana sauya manufofin kasafin kuɗin shugaban ƙasa zuwa kuɗaɗen da za a kashe bisa doka. Bamidele ya bayyana cewa kasafin na shekarar 2026 an tsara shi ne bisa sauye-sauyen tattalin arziki da ake aiwatarwa domin dawo da daidaito, gyara kura-kurai da ƙarfafa kuɗaɗen gwamnati.

Sanatan ya ƙara da cewa kasafin kuɗin 2026 ba gwaji ba ne, illa kasafi ne na ƙarfafa sauye-sauyen da aka fara, daidaita manyan alamomin tattalin arziki, da hanzarta ci-gaba ta hanyar saka hannun jari na gwamnati a muhimman fannoni.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata