DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tabarbarewar tsaro ba ta da alaka da gazawar jami’an tsaro sai dai siyasantar da matsalar – Rabi’u Kwankwaso

-

Jagoran Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce tabarbarewar tsaro a Nijeriya ba gazawar sojoji ba ce, illa dai rashin ƙwazon shugabannin siyasa.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a Kano yayin ƙaddamar da rundunar Kano State Neighbourhood Watch Corps da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa, inda aka gabatar da jami’ai 2,000 da aka horas domin taimakawa tsaron al’umma.

Google search engine

A cewarsa, sojojin Nijeriya jajirtattu ne kuma kwararru, amma abin da aka rasa shi ne ƙwazon siyasa, musamman daga Babban Kwamandan Rundunonin Tsaro, yana mai jaddada cewa gwamnati ta samar da kayan aiki, makamai da horo ga jami’an tsaro.

Tsohon Ministan Tsaron ya kuma yaba wa gwamnatin Kano kan kafa rundunar tsaron unguwanni, yana mai cewa mataki ne da ya dace domin fuskantar ƙalubalen tsaro, musamman a yankunan iyaka da makwabtan jihohin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai bukatar dole sai ‘yan kwallon Super Eagles sun inganta wasansu matukar suna son nasara – Eric Chelle

Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar...

Hukumar EFCC ta ki bin umurnin kotu inda ta ci-gaba da tsare Malami

Ofishin Abubakar Malami, SAN, ya yi tir da yadda EFCC ta ki bin umarnin kotun FCT Abuja na a saki Malami bayan ya cika sharuddan...

Mafi Shahara