Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBa da jimawa ba kwamitin majalisar wakilan Nijeriya zai kammala binciken dokokin...

Ba da jimawa ba kwamitin majalisar wakilan Nijeriya zai kammala binciken dokokin harajin da ake zargin an sauya

Kwamitin wucin-gadi na Majalisar Wakilai da ke binciken bambance-bambancen da ake zargi a cikin sabbin dokokin sauya haraji ya yanke shawarar kammala aikinsa da gabatar da rahotonsa ga majalisa cikin gaggawa.

An kafa kwamitin karkashin jagorancin Muktar Aliyu Betara (Borno, APC) bayan ɗan majalisa Abdulsammad Dasuki ya ɗaga batun kan rashin daidaito tsakanin dokokin da majalisar ta amince da su da kuma waɗanda aka wallafa a jaridar hukuma.

Kwamitin ya yi alkawarin gudanar da bincike cikin gaskiya da tsanaki, inda za a gabatar da sakamakon da shawarwari ga majalisar cikin dan lokaci bayan kammala binciken.

Dokokin da ake bincike a kansu sun haɗa da: Dokar Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa, Dokar Hukumar Hada-hadar Haraji ta Ƙasa, Dokar Gudanar da Haraji ta Nijeriya, da kuma Dokar Haraji ta Nijeriya, waɗanda aka amince da su a majalisar a watan Maris kuma Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu a kansu a watan Yuni.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata