Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaTinubu ne Malamina a siyasa - Shugaban APC na Nijeriya

Tinubu ne Malamina a siyasa – Shugaban APC na Nijeriya

Shugaban jam’iyyar APC na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda ya bayyana cewa yana koyon siyasa ne a wajen shugaba Tinubu.

Nentawe ya fadi hakan ne yayin da yake karbar sarautar gargajiya ta “Kaeh-rit” a jihar Plateau.

A cewar sa, shugaba Tinubu gogaggen dan siyasa ne wanda ya kasance cikin wadanda ya kamata a yi koyi da su a fagen siyasa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Haka kuma ya jingina duk wata nasara da zai iya samu a tafiyarsa ta siyasa do horon da ya samu daga Tinubu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata