Shugaban jam’iyyar APC na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda ya bayyana cewa yana koyon siyasa ne a wajen shugaba Tinubu.
Nentawe ya fadi hakan ne yayin da yake karbar sarautar gargajiya ta “Kaeh-rit” a jihar Plateau.
A cewar sa, shugaba Tinubu gogaggen dan siyasa ne wanda ya kasance cikin wadanda ya kamata a yi koyi da su a fagen siyasa, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Haka kuma ya jingina duk wata nasara da zai iya samu a tafiyarsa ta siyasa do horon da ya samu daga Tinubu.
