Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiKasar Birtaniya ta dakatar da bai wa 'yan Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo biza

Kasar Birtaniya ta dakatar da bai wa ‘yan Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo biza

Gwamnatin kasar Birtaniya ta sanar da dakatar da tsarin ba ’yan Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo biza, lamarin da ake zargin zai shafi matafiya daga ƙasar da dama.

Wannan mataki, kamar yadda hukumomin Birtaniya suka bayyana, ya biyo bayan kin karɓar ’yan ƙasar da suka shiga Birtaniya ba bisa ƙa’ida ba.

Baya ga haka, Birtaniya ta ce manyan jami’an gwamnati da manyan baki daga Congo za su rasa damar shiga kasar kamar yadda suka saba a baya.

Rahotanni sun nuna cewa a cikin watan Nuwamba, ma’aikatar cikin gida ta Birtaniya ta gargadi DR Congo, Angola da Namibia cewa za su fuskanci takunkumin biza matuƙar ba su karɓi ’yan gudun hijira da kuma ’yan ƙasarsu masu aikata laifuka a kasashen ƙetare ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata