‘Yan majalisar wakilai marasa rinjaye sun nuna bukatar gwamnatin Nijeriya ta dakatar da aiwatar da sabbin dokar gyaran haraji har sai an kammala bincike kan zargin cewa an yi wa dokokin sauye-sauye bayan majalisa ta amince da ita.
An bayyana wannan bukata ce a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi wacce Honarabul Kingsley Chinda tare da mataimakinsa Aliyu Madaki da George Ozodinobi suka sanya wa hannu.
’Yan majalisar sun bayyana cece-kucen da ke tattare da dokokin harajin a matsayin abin damuwa sosai, suna cewa ya cancanci cikakken bincike domin kare martabar majalisa da bin doka da oda.
