Jam’iyyar APC ta bukaci jam’iyyun adawa su daina magana marar amfani kan ziyarar da shugaba Tinubu ya kai ƙasashen Turai.
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ta a jihar Legas Seye Oladejo ya fitar a Litinindinnan yayin da yake mayar da martani ga sukar da jam’iyyar ADC ta yi kan tafiyar shugaban kasa.
Oladejo ya ce kalaman ’yan adawar na nuna rashin fahimta kan tsarin mulki na zamani da diflomasiyyar ƙasa da ƙasa.
