Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAPC a jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukuma

APC a jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukuma

Jam’iyyar APC a jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Birnin Kebbi kuma shugaban Ciyaman ALGON na jihar Dahiru Nayaya daga jam’iyyar bisa zargin aikata rashin da’a da saba wa ka’ida.

Dakatarwar na kunshe ne cikin wata sanarwa da Mataimakin shugaban APC na yankin Kebbi ta Tsakiya Abubakar Bello ya aikewa manema labarai.

A cewar takardar, jam’iyyar ta dauki matakin ne bayan samun rahotannin binciken cikin gida, wadanda suka danganta Dahiru Nayaya da yin wasu ayyukan da jam’iyyar ta ce suna barazana ga hadin kai da martabar APC.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata